Kasar Afrika ta Kudu na tuhumar mutumin da ya bankawa majalisar dokokin kasar wuta, a matsayin dan ta’adda.
A na tuhumar wanda a ke zargin a wata gobara da ta kone wasu sassan ginin majalisar dokokin kasar Afirka ta Kudu mai shekaru 138 da haihuwa.
Mutumin ya gurfana a gaban kotu kan karar da jami’an kasar su ka bayyana a matsayin wani hari ga dimokradiyyar kasar.
An tuhumar, Zandile Mafe mai shekaru 49 da laifin kona majalisar, sakamakon gobarar da ta tashi a ranar 2 ga watan Janairu, amma an kara tuhumar sa da laifin ta’addanci, saboda shima an kama shi da wani abu mai fashewa, in ji mai gabatar da kara.
An dage shari’ar har zuwa ranar 11 ga watan Fabrairu, kuma Mafe ya bayar da umarnin a tsare shi a cibiyar kula da masu tabin hankali, bayan rokon da majalisar tsaronsa ta yi masa na cewa yana fama da tabin hankali.