fidelitybank

Afrika su sake sabon nazari a kan demokradiyar Turawa – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obansanjo, ya shawarci al’ummar Afirka su sake nazarin tsarin dimokraɗiyyar da Turawan Yamma suka sakar musu.

Gidan talbijin na Channel a Najeriya, ya ambato mista Obasanjo na cewa dole ne ƙasashen Afirka su gina tsarin dimokraɗiyyar da zai dace da al’adu da ɗabi’un al’ummar yankin.

Mista Obasanjo ya bayyana hakan ne a wani taro kan dimokradiyyar nahiyar Afirka da aka gudanar a ɗakin taro na Yar’adua Centre da ke Abuja babban birnin ƙasar.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce lokaci ya yi da al’ummar Afirka za su ajiye tsarin da turawa suka gadar musu, su gina nasu wanda zai dace da ala’dunsu.

Ya kuma ce yana da kyau shugabannin Afirka su nuna kishi da kan ci gaban al’umominsu.

Obasanjo ya ce idan ana son dimokraɗiyya ya yi aiki a Najeriya da ma Afirka baki-ɗaya, dole ne a gina shi kan tsarin shugabanci na gari, ta hanyar bai wa doka ta yi aiki.

Tsohon shugaban ƙasar, ya sha sukar yadda ake gudanar da tsarin dimokraɗiyya a Najeriya da ma ƙasashen Afirka.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp