Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, Afirka ce ta fi kowace nahiya yawan mutanen da ke kashe kansu a fadin duniya.
A yanzu haka kungiyar ta kaddamar da wani gangamin yaki da ta’adar kashe kai a shafukan sada zumunta da muhawara a nahiyar, domin wayar da kan jama’a da karfafa daukar matakai.
A cikin wata sanarwa hukumar ta WHO ta ce kasashen Afrika 6 na cikin jerin kasashe 10 da suke da yawan masu kashe kan nasu a duniya.
Hukumar ta kuma ce likitan kwakwalwa 1 ne ke duba lafiyar mutane rabin miliyan a nahiyar ta Afrika- adadin da ya nunka shawarar masana da kashi 100 cikin 100.
Hukumar ta lura da cewa matsalar kwakwalwa ita ce babbar matsala da kashi 10 cikin 100 da ke janyo kashe kai – kuma a nahiyar Afrika kusan daukacin masu aikin jinya na kwakwalwa a birane suke.
Shugaban ofishin hukumar a Afrika, Dr. Matshidiso Moeti ya ce matsalar da ke janyo mutum ya kashe kansa matsala ce da za a iya magance ta amma kuma galibin gwamnatoci ba sa mayar da hankali a kai.
An kaddamar da gangamin na kafafen shafukan intanet ne gabanin ranar lura da lafiyar kwakwalwa ta duniya da za a gudanar a ranar 10 ga watan nan na Oktoba.
Manufar hukumar ta lafiya ta duniya ita ce yekuwarta ta kai ga mutum miliyan 10 a nahiyar Afrika. In ji BBC.