fidelitybank

Afrika ka ce a kan gaba wajen da mutane ke kashe kansu

Date:

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, Afirka ce ta fi kowace nahiya yawan mutanen da ke kashe kansu a fadin duniya.

A yanzu haka kungiyar ta kaddamar da wani gangamin yaki da ta’adar kashe kai a shafukan sada zumunta da muhawara a nahiyar, domin wayar da kan jama’a da karfafa daukar matakai.

A cikin wata sanarwa hukumar ta WHO ta ce kasashen Afrika 6 na cikin jerin kasashe 10 da suke da yawan masu kashe kan nasu a duniya.

Hukumar ta kuma ce likitan kwakwalwa 1 ne ke duba lafiyar mutane rabin miliyan a nahiyar ta Afrika- adadin da ya nunka shawarar masana da kashi 100 cikin 100.

Hukumar ta lura da cewa matsalar kwakwalwa ita ce babbar matsala da kashi 10 cikin 100 da ke janyo kashe kai – kuma a nahiyar Afrika kusan daukacin masu aikin jinya na kwakwalwa a birane suke.

Shugaban ofishin hukumar a Afrika, Dr. Matshidiso Moeti ya ce matsalar da ke janyo mutum ya kashe kansa matsala ce da za a iya magance ta amma kuma galibin gwamnatoci ba sa mayar da hankali a kai.

An kaddamar da gangamin na kafafen shafukan intanet ne gabanin ranar lura da lafiyar kwakwalwa ta duniya da za a gudanar a ranar 10 ga watan nan na Oktoba.

Manufar hukumar ta lafiya ta duniya ita ce yekuwarta ta kai ga mutum miliyan 10 a nahiyar Afrika. In ji BBC.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp