fidelitybank

Afirka ta Kudu za ta ɗaukaka ƙara kan sakin limamin kiristan Najeriya da ake zargi da yin fyaɗe

Date:

Hukumomin ƙasar Afirka ta kudu sun ce za su ci gaba da bin matakan shari’a domin tabbatar da an sake gurfanar da limamin kirastan nan mai da’awa ta kafar talabijin Timothy Omotoso wanda a watan da ya wuce wata kotu ta wanke shi daga zargin yin fyaɗe, duk kuwa da cewa ba ya cikin ƙasar a yanzu.

Mista Omotoso dai ya musanta zarge-zarge har 32 da aka yi masa ciki kuwa har da cin zarafin wata matashiya ta hanyar lalata, a wata mujami’arsa da ke birnin Port Elizabeth.

Hukumar da ta shigar da ƙara a Afirka ta kudun (NPA) ta sha alwashin ɗaukaka ƙarar, inda ta ce ko da Mista Omotoso ba ya cikin ƙasar hakan ba zai hana ɗaukar matakin ba.

Hakazalika, idan har ta samu wannan nasara, gwanatin ƙasar za ta nemi Najeriya ta mayar da Mista Omotosho ƙasar domin fuskantar hukuncin, kasancewar ƙasashen biyu na da kyakkyawar hulɗar diflomasiya tsakanin su.

Bayan da wata kotu ƙasar ta wanke shi daga zarge-zargen a watan Afrilun da ya gabata, limamin kiristan na kuma fuskantar ƙarin tuhuma bisa dalilan shiga ƙasar ba tare da izini ba, kasancewar an dakatar da shi daga shiga Afirka ta kudu har na sawon shekara biyar.

Timothy Omotoso dai na jagorantar mujami’ar Jesus Dominion ta duniya wadda ke da rassa a ƙasashen Birtaniya da Najeriya da Faransa da Isra’ila da kuma Afirka ta kudu.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp