fidelitybank

Afirka ta Kudu za ta ɗaukaka ƙara kan sakin limamin kiristan Najeriya da ake zargi da yin fyaɗe

Date:

Hukumomin ƙasar Afirka ta kudu sun ce za su ci gaba da bin matakan shari’a domin tabbatar da an sake gurfanar da limamin kirastan nan mai da’awa ta kafar talabijin Timothy Omotoso wanda a watan da ya wuce wata kotu ta wanke shi daga zargin yin fyaɗe, duk kuwa da cewa ba ya cikin ƙasar a yanzu.

Mista Omotoso dai ya musanta zarge-zarge har 32 da aka yi masa ciki kuwa har da cin zarafin wata matashiya ta hanyar lalata, a wata mujami’arsa da ke birnin Port Elizabeth.

Hukumar da ta shigar da ƙara a Afirka ta kudun (NPA) ta sha alwashin ɗaukaka ƙarar, inda ta ce ko da Mista Omotoso ba ya cikin ƙasar hakan ba zai hana ɗaukar matakin ba.

Hakazalika, idan har ta samu wannan nasara, gwanatin ƙasar za ta nemi Najeriya ta mayar da Mista Omotosho ƙasar domin fuskantar hukuncin, kasancewar ƙasashen biyu na da kyakkyawar hulɗar diflomasiya tsakanin su.

Bayan da wata kotu ƙasar ta wanke shi daga zarge-zargen a watan Afrilun da ya gabata, limamin kiristan na kuma fuskantar ƙarin tuhuma bisa dalilan shiga ƙasar ba tare da izini ba, kasancewar an dakatar da shi daga shiga Afirka ta kudu har na sawon shekara biyar.

Timothy Omotoso dai na jagorantar mujami’ar Jesus Dominion ta duniya wadda ke da rassa a ƙasashen Birtaniya da Najeriya da Faransa da Isra’ila da kuma Afirka ta kudu.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp