fidelitybank

Afirka ta Kudu za ta ɗaukaka ƙara kan sakin limamin kiristan Najeriya da ake zargi da yin fyaɗe

Date:

Hukumomin ƙasar Afirka ta kudu sun ce za su ci gaba da bin matakan shari’a domin tabbatar da an sake gurfanar da limamin kirastan nan mai da’awa ta kafar talabijin Timothy Omotoso wanda a watan da ya wuce wata kotu ta wanke shi daga zargin yin fyaɗe, duk kuwa da cewa ba ya cikin ƙasar a yanzu.

Mista Omotoso dai ya musanta zarge-zarge har 32 da aka yi masa ciki kuwa har da cin zarafin wata matashiya ta hanyar lalata, a wata mujami’arsa da ke birnin Port Elizabeth.

Hukumar da ta shigar da ƙara a Afirka ta kudun (NPA) ta sha alwashin ɗaukaka ƙarar, inda ta ce ko da Mista Omotoso ba ya cikin ƙasar hakan ba zai hana ɗaukar matakin ba.

Hakazalika, idan har ta samu wannan nasara, gwanatin ƙasar za ta nemi Najeriya ta mayar da Mista Omotosho ƙasar domin fuskantar hukuncin, kasancewar ƙasashen biyu na da kyakkyawar hulɗar diflomasiya tsakanin su.

Bayan da wata kotu ƙasar ta wanke shi daga zarge-zargen a watan Afrilun da ya gabata, limamin kiristan na kuma fuskantar ƙarin tuhuma bisa dalilan shiga ƙasar ba tare da izini ba, kasancewar an dakatar da shi daga shiga Afirka ta kudu har na sawon shekara biyar.

Timothy Omotoso dai na jagorantar mujami’ar Jesus Dominion ta duniya wadda ke da rassa a ƙasashen Birtaniya da Najeriya da Faransa da Isra’ila da kuma Afirka ta kudu.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp