Hukumomin Taliban a Afganistan sun fitar da wata doka da ta hana masu sana’ar aski yin aski ko yanke gemu ga maza, inda su ka kara da cewa haramun ne a Musulunci.
Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan da mahukuntan Taliban na Afganistan su ka sanya dokar hana zirga-zirga a kan mata dole sai da muharramin su.
Muryar Amurka ta samu kwafin umarnin da ma’aikatar kula da nagarta da rigakafin ta’addanci ta fitar a wannan makon.
Wani jami’in Taliban ya raba ainihin tsari a cikin harshen Pashto; duk da haka manyan shugabanni ba su tabbatar da sahihancin sa ba.
Lokacin da Muryar Amurka ta tuntubi kakakin Taliban, Zabihullah Mujahid, bai musanta sahihancin umarnin ba, amma ya ce har yanzu ya na “kokarin samun bayanai” game da dokar.
Umarnin ya nakalto ayoyi da dama daga Alqur’ani da hadisai, game da bin duk abin da Annabi Muhammad (S.A.W) ya umuaci musulmi su yi.
“Tsarin gemu aiki ne na dabi’a kuma Sunna (hanyar rayuwa da tafarki na shari’a) na dukkan Annabawa da Shari’ar Musulunci sun sha jaddada shi,” in ji umarnin.
Ministan yada kyawawan dabi’u, Sheikh Muhammad Khalid Haqqani ne ya sanya wa hannu kan wannan umarni.
“Aski ko yanke gemu haramun ne a karkashin shawarar da malaman addini su ka yi gaba daya. Sahabban Annabi Muhammadu (S.A.W) da mabiyansu da magadan bayansu da Mujahidai [Jarumai tsarkaka] da sauran malamai ba su yi ittifaqi a kan aske ko aski ba.
“Domin haka, an fahimci cewa aski ko yanke gemu ya saba wa dabi’ar dan Adam, kuma matakin ya saba wa Shari’ar Musulunci,” a cewar umarnin.
“Saboda abin da ya gabata, a na sanar da duk masu yin aski da su kiyaye Shari’ar Musulunci da umarnin Musulunci yayin yanke gashi da yi wa abokan cinikinsu hidima.”
Ga dukkan alamu wannan umarni ya tsaya cik kan dokar hana sassauta gemu da kungiyar Taliban ta bayar a lokacin gwamnatinsu ta karshe daga 1996 zuwa 2001. Jami’an Taliban sun ce kungiyar na kokarin karfafawa ‘yan kasar ta Afganistan kwarin gwiwa, wajen daukar tsauraran ra’ayin addinin Musulunci.
“Dukkan sassan larduna da ke karkashin ma’aikatar an umarce su da cewa, tsayar da gemu daya ne daga cikin Sunnar Annabi Muhammadu (S.A.WA), kuma dukkan Musulmi su bi Sunnar Annabi Muhammadu (S.A.W). Haka nan kuma an umarci dukkan ma’aikatan aski da ke larduna da su kiyaye umarnin yayin da su ke yanke gemu na kwastomomi.”
“Ya kamata jami’a su yi kokarin aiwatar da wannan dokar cikin ladabi da mutuntawa, domin haka ‘yan kasar su yi rayuwarsu daidai da addininsu, wajibcin Musulunci da Sunnar Annabi Muhammadu (S.A.W)”. A cewar umarnin.
“An aiko muku da waɗannan umarnin, doMIn aiwatarwa.”
Sai dai kuma masu aski a Kabul sun ce mutane da yawa ba sa son aske gemu tun kafin Taliban ta fitar da wannan doka.
Wani mai aski a wani shagon Kabul ya shaidawa Muryar Amurka cewa, a farkon watan Disamba yak an yi aski kashi 20 cikin 100 na kasuwancin da ya ke yi a baya tun bayan da ‘yan Taliban su ka karbe birnin.
‘Yan Taliban sun kwace iko da babban birnin Afganistan a tsakiyar watan Agusta. Tun daga wannan lokacin su ka fara gabatar da shari’o’in Musulunci tare da haramta cudanya da tarbiyyar maza da mata.