fidelitybank

Afghanistan: Dalilan gwamnatin Taliban a kan hana aske Gemu

Date:

Hukumomin Taliban a Afganistan sun fitar da wata doka da ta hana masu sana’ar aski yin aski ko yanke gemu ga maza, inda su ka kara da cewa haramun ne a Musulunci.

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan da mahukuntan Taliban na Afganistan su ka sanya dokar hana zirga-zirga a kan mata dole sai da muharramin su.

Muryar Amurka ta samu kwafin umarnin da ma’aikatar kula da nagarta da rigakafin ta’addanci ta fitar a wannan makon.

Wani jami’in Taliban ya raba ainihin tsari a cikin harshen Pashto; duk da haka manyan shugabanni ba su tabbatar da sahihancin sa ba.

Lokacin da Muryar Amurka ta tuntubi kakakin Taliban, Zabihullah Mujahid, bai musanta sahihancin umarnin ba, amma ya ce har yanzu ya na “kokarin samun bayanai” game da dokar.

Umarnin ya nakalto ayoyi da dama daga Alqur’ani da hadisai, game da bin duk abin da Annabi Muhammad (S.A.W) ya umuaci musulmi su yi.

“Tsarin gemu aiki ne na dabi’a kuma Sunna (hanyar rayuwa da tafarki na shari’a) na dukkan Annabawa da Shari’ar Musulunci sun sha jaddada shi,” in ji umarnin.

Ministan yada kyawawan dabi’u, Sheikh Muhammad Khalid Haqqani ne ya sanya wa hannu kan wannan umarni.

“Aski ko yanke gemu haramun ne a karkashin shawarar da malaman addini su ka yi gaba daya. Sahabban Annabi Muhammadu (S.A.W) da mabiyansu da magadan bayansu da Mujahidai [Jarumai tsarkaka] da sauran malamai ba su yi ittifaqi a kan aske ko aski ba.

“Domin haka, an fahimci cewa aski ko yanke gemu ya saba wa dabi’ar dan Adam, kuma matakin ya saba wa Shari’ar Musulunci,” a cewar umarnin.

“Saboda abin da ya gabata, a na sanar da duk masu yin aski da su kiyaye Shari’ar Musulunci da umarnin Musulunci yayin yanke gashi da yi wa abokan cinikinsu hidima.”

Ga dukkan alamu wannan umarni ya tsaya cik kan dokar hana sassauta gemu da kungiyar Taliban ta bayar a lokacin gwamnatinsu ta karshe daga 1996 zuwa 2001. Jami’an Taliban sun ce kungiyar na kokarin karfafawa ‘yan kasar ta Afganistan kwarin gwiwa, wajen daukar tsauraran ra’ayin addinin Musulunci.

“Dukkan sassan larduna da ke karkashin ma’aikatar an umarce su da cewa, tsayar da gemu daya ne daga cikin Sunnar Annabi Muhammadu (S.A.WA), kuma dukkan Musulmi su bi Sunnar Annabi Muhammadu (S.A.W). Haka nan kuma an umarci dukkan ma’aikatan aski da ke larduna da su kiyaye umarnin yayin da su ke yanke gemu na kwastomomi.”

“Ya kamata jami’a su yi kokarin aiwatar da wannan dokar cikin ladabi da mutuntawa, domin haka ‘yan kasar su yi rayuwarsu daidai da addininsu, wajibcin Musulunci da Sunnar Annabi Muhammadu (S.A.W)”. A  cewar umarnin.

“An aiko muku da waɗannan umarnin, doMIn aiwatarwa.”

Sai dai kuma masu aski a Kabul sun ce mutane da yawa ba sa son aske gemu tun kafin Taliban ta fitar da wannan doka.

Wani mai aski a wani shagon Kabul ya shaidawa Muryar Amurka cewa, a farkon watan Disamba yak an yi aski kashi 20 cikin 100 na kasuwancin da ya ke yi a baya tun bayan da ‘yan Taliban su ka karbe birnin.

‘Yan Taliban sun kwace iko da babban birnin Afganistan a tsakiyar watan Agusta. Tun daga wannan lokacin su ka fara gabatar da shari’o’in Musulunci tare da haramta cudanya da tarbiyyar maza da mata.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...
X whatsapp