Sengal ta baiwa tawagar ‘yan wasan ƙasar da suka lashe gasar Kofin nahiyar Afirka da kyautuka filiye.
Kowane ɗan wasa ya samu kyautar dala 87,000 (fiye da Naira miliyan 36) haɗi da fili a cikin birnin Dakar da kuma Diamniadio yayin wani biki a fadar shugaban ƙasa.
Shugaban Kasa, Macky Sall, ya kuma girmama tawagar da lambar yabo ta Order of the Lion.
Tun farko shugaban ya gode wa tawagar saboda kai wa “matsayin ƙololuwa a Afirka” da kuma “samo wa manyan mutane girmamawa”.
Ya kuma yi yabo na musamman ga kocin tawagar, Aliou Cissé.
Senegal ta doke Egypt 4-2 a bugun daga kai sai mai tsaron raga kafin ta lashe kofin a karon farko a tarihi.