Mai horas da tawagar Super Eagles, Augustine Eguavoen ya fitar da jerin sunayen ‘yan wasan Najeriya wanda za su buga gasar cin kofin nahiyar Afrika karo na 33 da za a yi a kasar Kamaru daga ranar 9 ga watan Janairu zuwa 6 ga Fabrairu, 2022.
Masu tsaron gida akwai Maduka Okoye da Francis Uzoho da masu tsaron baya Kenneth Omeruo da Olaoluwa Aina da Abdullahi Shehu da ‘yan wasan tsakiya Joseph Ayodele-Aribo da Chidera Ejuke da ‘yan wasan gaba Moses Simon da Odion Ighalo da Samuel Chukwueze suma suna cikin jerin sunayen.
A na sa ran dukkan ‘yan wasan da a ka gayyata, za su isa sansani a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja ranar 29 ga watan Disamba, inda a ke sa ran ‘yan wasan da ke Burtaniya za su fara isowa ranar Litinin, 3 ga watan Janairu.
Masu tsaron gida: Francis Uzoho (AC Omonia, Cyprus); John Noble (Enyimba FC); Daniel Akpeyi (Kaizer Chiefs, Afirka ta Kudu); Maduka Okoye (Sparta Rotterdam, Netherlands)
Masu tsaron baya: Chidozie Awaziem (Alanyaspor FC, Turkiyya); Kenneth Omeruo (CD Leganes, Spain); Leon Balogun (Glasgow Rangers, Scotland); William Ekong (Watford FC, Ingila); Olaoluwa Aina (Torino FC, Italiya); Jamilu Collins (SC Padeborn 07, Jamus); Abdullahi Shehu (AC Omonia, Cyprus); Zaidu Sanusi (FC Porto, Portugal); Olisa Ndah (Orlando Pirates, Afirka ta Kudu).
‘Yan wasan tsakiya: Frank Onyeka (Brentford FC, Ingila); Joseph Ayodele-Aribo (Galsgow Rangers, Scotland); Wilfred Ndidi (Leicester City, Ingila); Chidera Ejuke (CSKA Moscow, Rasha); Kelechi Nwakali (SD Huesca, Spain)
‘Yan wasan gaba: Ahmed Musa (Fatih Karagumruk, Turkiyya); Samuel Chukwueze (Villarreal FC, Spain); Victor Osimhen (Napoli FC, Italiya); Moses Simon (FC Nantes, Faransa); Sadiq Umar (UD Almeria, Spain); Taiwo Awoniyi (Union Berlin, Jamus); Odion Jude Ighalo (Al-Shabab Riyadh, Saudi Arabia); Alex Iwobi (Everton FC, Ingila); Kelechi Iheanacho (Leicester City, Ingila); Emmanuel Dennis (Watford FC, Ingila).