Sakamakon dukkanin wasannin da aka buga a gasar cin kofin nahiyar Afirka, AFCON na shekarar 2025, da aka buga ranar Litinin.
Super Eagles ta Najeriya ta kasa doke Rwanda a wasan karshe na rukunin D a filin wasa na Godswill Akpabio International Stadium, Uyo.
Zakarun Afirka sau uku sun sha kashi da ci 2-1 a bayan gida.
A wani wasan da aka buga ranar litinin, Morocco ta lallasa Lesotho da ci 7-0 yayin da Ghana ta sha kashi a hannun Nijar da ci 2-1 a gida.
Libya ta buga 0-0 da Jamhuriyar Benin, sannan Angola kuma ta buga 0-0 da Sudan.
Ga cikakken sakamakon wasannin share fage na AFCON 2025 da aka buga ranar Litinin:
Najeriya 1-2 Rwanda
Ghana 1-2 Niger
Morocco 7-0 Lesotho
Sudan 0-0 Angola
Libya 0-0 Jamhuriyar Benin
Tunisia 0-1 Gambia
Comoros 1-0 Madagascar
CAR 0-1 Gabon
Malawi 3-0 Burkina Faso.
A halin da ake ciki, a yau Talata ne za a yi karin wasannin share fage na AFCON.
Kenya za ta karbi bakuncin Namibia, Tanzania za ta kara da Guinea, Kamaru za ta kara da Zimbabwe, yayin da Masar za ta kara da Botswana.