A ranar 9 ga watan Junairu 2022 ne dai a ka tsara fara gasar cin kofin kasashe na nahiyar Arfika mai taken “AFCON” a kasar Kamaru, amma tuni hukumar kungiyoyin nahiyar Turai ECA ta bayyana rashin son sakin ‘yan wasa su tunkari gasar.
Sai dai kuma da ya ke mayar da martani kan hakan, Adebayor, wanda ya taba bugawa Arsenal da Tottenham wasa, ya caccaki hukumar ECA kan kin sakin ‘yan wasan da za su buga gasar AFCON.
“Babu wani koci a duniya da zai hana ni buga wasa a AFCON, abin kyama ne yadda wasu ke kokarin hana ‘yan wasan Afirka taka leda a AFCON,” kamar yadda ya shaida wa BBC Sport.
A kwanakin baya ne dai aka samu rahotannin cewa za a iya soke gasar ta AFCON, sai dai shugaban hukumar ta CAF Patrice Mostepe ya tabbatar da cewa gasar za ta gudana kamar yadda aka tsara.