Shugaban Bankin Raya Afirka, AfDB, Akinwumi Adesina ya shiga takarar neman tikitin shugaban kasa a jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
Hakan ya faru ne saboda gamayyar kungiyoyi 28 da suka kunshi Youth Arise Movement, Nigerians in Diaspora, One Nigeria Group, Prudent Youth Association of Nigeria, kungiyoyin mata, manoma, nakasassu da sauran kungiyoyin fararen hula, sun tara kudi Naira miliyan 100, don siyan fom din takarar shugaban kasa da bayyana sha’awar tsohon ministan noma.
Gamayyar dai na karkashin jagorancin shugaban kungiyar, Mohammed Saleh. Matakin dai ya haifar da cece-ku-ce na tsawon makonni da dama da ake yi cewa, wasu jiga-jigan jam’iyyar APC na kara matsa lamba kan Adesina ya shiga takarar, kuma zai yi sauki a samu amincewar shugaban kasa kan takararsa.
A wani labarin kuma, Darakta Janar na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Hon. Abdulmumin Jibrin, ya fice daga jam’iyya mai mulki.
Abdulmumin ya bayyana ficewarsa daga APC ne a shafin sa na Facebook, cewa nan da sa’a 24 zai bayyana sabuwar jam’iyyar da zai koma.