Ɗan wasan ƙwallon ƙafa na tawagar Super Eagles ta Najeriya da ƙungiyar Atalanta ta Italiya, Ademola Lookman ya lashe kyautar ɗan ƙwallon ƙafa na Afirka.
Ɗan wasan ya doke fitattun zaratan ƴan wasa irin Achraf Hakimi na Morocco da Simon Adingra na tawagar Ivory Coast da ƙungiyar Brighton & Hove Albion ta Ingila da Ruto Williams na Afirka ta Kudu da Serhou Guirassy na ƙasar Guinea da ƙungiyar Dortmund ta Jamus domin lashe kyautar.
An gudanar da bikin karrama gwarazan ƴanwasan na Afrika ne a a birnin Marrakech na ƙasar Morocco.
Lashe kyautar a wannan karon ya sa ƴan wasan Najeriya biyu sun lashe kyautar sau biyu a jere bayan Victor Osimhen da ya lashe kyautar a bara.