fidelitybank

Adeleke ya kafa kwamitin da zai kwato kadarorin jihar Osun

Date:

Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun, ya kaddamar da Kwamitin karkashin jagorancin, Dr Muyiwa Oladimeji wanda zai bibiyi yadda zai kwato kadarorin jihar da aka wawushe.

Kwamitin da zai tattara kadarori da kwato kadarorin Jiha, wanda B.T. Salam ya jagoranta; Kwamitin Bitar Kwangiloli, karkashin jagorancin Mista Niyi Owolade da Kwamitin binciken Al’amuran Mulki.

Ya dora musu alhakin bin diddigin duk wasu kadarorin gwamnati da aka wawashe na jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Adeleke, Malam Olawale Rasheed, ya fitar a ranar Laraba.

Gwamnan ya ba da wannan umarni ne bayan kaddamar da wasu bangarori hudu a Osogbo domin su kuma duba duk nade-naden da gwamnatin da ta gabata ta yi bayan ranar 17 ga watan Yuli.

Adeleke, wanda mataimakin gwamnan jihar, Mista Kola Adewusi ya wakilta, ya yi tir da yadda ake “watse” kadarorin gwamnati.

“Dole ne ku gyara kurakuran ku kuma ku sauke nauyin da aka dora muku cikin gaggawa.
“Muna tabbatar wa da jama’a cewa ba za mu yi kasa a gwiwa ba a kan kudurinmu na dakatar da duk wasu laifukan da suka saba wa doka bayan 17 ga watan Yuli,” in ji shi, inda ya ba da tabbacin cewa albashin jihar kafin ranar 17 ga watan Yuli yana nan daram.
Adeleke ya ce gwamnatin jihar ba ta kori wani ma’aikaci da ke karbar albashin Osun ba.
“Wadanda ke da al’amuran da za su yi bayani su ne wadanda suka shiga lissafin albashi bayan 17 ga Yuli,” in ji shi.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...

Kwallaye 6 da aka zurawa Santos a raga ta sanya Neymar ya fashe da kuka

Ɗan wasan tawagar Brazil, Neymar ya fice daga cikin...

Hukumar Shari’a ta magantu kan sadakin dubu 20 da ya yamutsa hazo a Kano

Hukumar shari’a ta jihar Kano, ta ce ba a...
X whatsapp