fidelitybank

Adeleke ne halastaccen gwamnan Osun – Kotu

Date:

Kotun daukaka kara ta tabbatar da Sanata Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya yi nasara a zaben gwamnan jihar Osun na ranar 16 ga watan Yuli 2022.

Da wannan hukuncin kotun wadda ta zauna a Abuja ta soke hukuncin da kotun sauraron kararrakin zaben gwamna ta jihar ta yi, wadda ta zartar da cewa ba shi ne ya yi nasara ba, abokin hamayyarsa na APC Gboyega Oyetola ne ya ci zaben.

A hukuncin da kotun ta farko ta yi, ta zartar da cewa dan takarar na PDP ba shi ne ya samu mafi rinjayen kuri’u ba, saboda haka ta umarci hukumar zabe ta karbe takardar shedar zaben da ta bai wa Adeleke, ta mika wa Oyetola.

To sai dai a wannan hukuncin na kotun daukaka karar, wanda alkalan kotun uku bisa jagorancin mai shari’a Mohammaed Shu’aibu duka bakinsu ya zo daya, ta soke wancan hukuncin kotun sauraron kararrakin gwamnan, inda ta ce

Adeleke shi ne halastaccen gwamnan jihar ta Osun.

Kotun daukaka karar ta ce kotun ta baya ba ta yi daidai ba da ta ce an yi aringizon kuri’u, wanda wannan ikirari ne da ta ce kotun ta dogara ne ga shedar da Oyetola da APC suka gabatar, wanda kuma wannan ba abin dogaro ba ne da ya tabbatar da ikirarin nasu.

Alkalin ya ce hakan ba daidai ba ne domin Oyetola da APC sun dogara ne ga bayanan da suke cikin na’ura ba tare da sun duba ainahin rijistar masu zabe ba, wadda ita ce dukkanin ainahin al’amuran zaben suka dogara da ita.

Saboda haka ba su da wata shaida da za ta tabbatar da zargin da suke yi na aringizon kuri’u.

Dangane da batun hurumin kotun daukaka karar na sauraron shari’ar, a nan ma ta zartar da hukuncin da ya yi wa Adeleke dadi, inda ta zartar da cewa bisa sashe na 285(8) na tsarin mulkin Najeriya, tana da dukkanin dama ta sauraron karar da aka daukaka.

Haka kuma kotun ta umarci dan takarar na APC Gboyega Oyetola da jam’iyyar tasa su biya tarar naira dubu 500 kan ɓata wa kotu lokaci

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp