Tsohon shugaban jam’iyyar All Progressives Congress APC na kasa, Kwamared Adams Oshiomhole, ya bayyana tsayawa takarar Sanatan Edo ta Arewa a hukumance a karkashin jam’iyyar APC.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da jagoran jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, kuma dan takarar shugaban kasa, Asiwaju Bola Tinubu, ya taya Adams Oshiomhole murna.
Oshiomhole ya kasance shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Edo. Ya cika shekaru 70 a yau.
A cikin wani sako da ofishin yada labaran sa ya rabawa manema labarai a ranar Litinin a Abuja, Tinubu ya ce, ya yi murna da Oshiomhole, saboda muhimmiyar gudunmawar da ya bayar wajen tabbatar da dimokuradiyya, shugabanci nagari da kuma ci gaban al’umma mai adalci ta hanyar fafutukar kare hakkin ma’aikata.