Jihar Adamawa ta sanar da kawo karshen barkewar cutar amai da gudawa, bayan da ba a gano wani mutum da ake zargi da kamuwa da cutar ba duk da ‘tsarin sa ido’ na makonni.
Kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Isa Abdulahi ne ya bayyana hakan a jiya yayin da yake zantawa da manema labarai a ofishin sa da ke Yola.
Abdulahi ya ce, cutar ta zo karshe ne bayan ta kama mutane 1,959 kuma ta yi sanadiyar mutuwar mutane 55.
Ya tuna cewa, an sanar da bullar cutar kwalara a watan Yulin bara, kuma a cikin watannin da suka biyo baya an samu jimillar mutane 1,959 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara.