Hukumar kiyaye hadurra ta kasa FRSC reshen jihar Kaduna, ta ce adadin wadanda suka mutu a hatsarin motan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja ya karu zuwa 18, tare da jikkata wasu 27.
Mista Kabir Nadabo, Kwamandan sashin ne ya tabbatar da hakan a wani karin bayani ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN).
Da sanyin safiyar Lahadin da ta gabata ne dai rundunar ta tabbatar da cewa mutane 16 ne suka mutu sannan wasu 27 suka samu raunuka sakamakon afkuwar lamarin.
A cewar Nadabo, hadarin ya faru ne da karfe 05:20 na safe a kan babbar hanyar da ke kusa da unguwar Audu Jangon.
Ya bayyana cewa, abubuwan da suka haddasa hadarin sun hada da gudu da kuma yawan lodin kaya da fasinjoji, lamarin da ya yi sanadin yawan wadanda abin ya shafa.
“Binciken da muka gudanar a kan lamarin ya nuna cewa mutane 65 ne suka shiga cikin hatsarin, 27 sun samu raunuka, 18 kuma sun mutu,” in ji Nadabo.
A cewarsa, rundunar ta Corps Marshal na FRSC ta samar da wasu tsare-tsare a fadin kasar nan a shekarun baya-bayan nan domin tabbatar da daukar matakan gaggawa kan hadurran ababen hawa, musamman a muhimman hanyoyin kasar nan.