fidelitybank

Adadin mutanen da suka rasu a titin Kaduna zuwa Abuja ya karu zuwa 18 – FRSC

Date:

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa FRSC reshen jihar Kaduna, ta ce adadin wadanda suka mutu a hatsarin motan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja ya karu zuwa 18, tare da jikkata wasu 27.

Mista Kabir Nadabo, Kwamandan sashin ne ya tabbatar da hakan a wani karin bayani ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN).

Da sanyin safiyar Lahadin da ta gabata ne dai rundunar ta tabbatar da cewa mutane 16 ne suka mutu sannan wasu 27 suka samu raunuka sakamakon afkuwar lamarin.

A cewar Nadabo, hadarin ya faru ne da karfe 05:20 na safe a kan babbar hanyar da ke kusa da unguwar Audu Jangon.

Ya bayyana cewa, abubuwan da suka haddasa hadarin sun hada da gudu da kuma yawan lodin kaya da fasinjoji, lamarin da ya yi sanadin yawan wadanda abin ya shafa.

“Binciken da muka gudanar a kan lamarin ya nuna cewa mutane 65 ne suka shiga cikin hatsarin, 27 sun samu raunuka, 18 kuma sun mutu,” in ji Nadabo.

A cewarsa, rundunar ta Corps Marshal na FRSC ta samar da wasu tsare-tsare a fadin kasar nan a shekarun baya-bayan nan domin tabbatar da daukar matakan gaggawa kan hadurran ababen hawa, musamman a muhimman hanyoyin kasar nan.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp