Gwamnan jihar Jigawa ta ce mutanen da suka mutu sakamakon fashewar tankar mai sun ƙaru zuwa 170.
Gwamnan jihar Malam Umar Namadi shi ya bayyana wa BBC hakan, inda ya ce ƙarin wadanda suka rasun masu jinya ne a asibiti, waɗanda tuni ‘yan’uwansu suka ɗauki gawawwakin tare da yi musu sutura.
Malam Namadi ya ce akwai ƙarin mutane 76 da suke kwance a asibitocin jihar da na birnin Nguru na jihar Yobe mai makobtaka.
Hatsarin ya faru ne ranar Talata da daddare a garin Majiya na ƙaramar hukumar Taura na jihar ta Jigawa.