Alƙaluman mutanen da girgizar ƙasa ta yi sanadiyyar mutuwarsu a Myanmar yanzu haka sun kai 2,719, kamar yadda shugaban sojoji, Min Aung Hlaing ya shaida a wani jawabi a gidan talbijin na ƙsar a ranar Talata.
Yawan mutunen kuma da suka samu raunuka sun kai 4,521 inda kuma har yanzu ba a ga mutum 441 ba.
Min Aung Hlaing ya ƙara da cewa akwai yiwuwar alƙaluman ka iya ƙaruwa zuwa 3,000.
A can kuma birnin Bangkok na ƙasar Thailand an kuma samun ƙarin gawar mutum guda sakamakon rushewar wani gini mai tsayi inda yanzu haka ake da ƙididdigar mutuwar mutum 14.