Adadin wadanda suka mutu a wani bene mai hawa uku da ya ruguje a Ebute-Meta a Legas ya kai 8, kamar yadda wani jami’i ya bayyana.
Ibrahim Farinloye, Ko’odinetan shiyyar Kudu-maso-Yamma, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ya yi magana da Kamfanin Dillancin Labarai na kasa NAN a ranar Litinin a Legas.
NAN ta ruwaito cewa, mutane takwas da suka mutu sun hada da maza biyar da mata uku.
Wani tsohon gini mai hawa uku ya ruguje a lamba 24 titin Ibadan, kusa da Herbert Macaulay Way, Ebute-Meta a daren Lahadi.
Lamarin ya faru ne a lokacin da mazauna garin suka kwanta barci kamar yadda NEMA ta bayyana.
Hukumar kashe gobara ta jihar Legas a wata sanarwa da ta fitar ta ce an sanar da su rugujewar jirgin da karfe 9:48 na dare.
Sanarwar ta kara da cewa jami’an kashe gobara da jami’an hukumar kula da gine-gine ta jihar Legas da kuma jami’an hukumar daukar marasa lafiya ta jihar Legas sun yi tattaki zuwa wurin.