fidelitybank

Abuwan da muke so masu zanga-zanga su gabatar mana kafin fara ta – ‘Yansanda

Date:

Yayin da wasu ‘yan Najeriya ke shirin gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa ranar 1 ga watan Agusta, rundunar ‘yan sandan ƙasar ta buƙaci masu shiga zanga-zangar su gabatar mata da sunaye da cikakkun bayanansu.

Babban Sifeton ‘yansandan ƙasar, Koyode Egbetokun ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja bababn birnin ƙasar.

Ya ƙara da cewa duk ƙungiyoyin da ke da muradin shiga zanga-zangar su gabatar da sunaye da cikakkun bayanansu ga kwamishinonin ‘yansandan jihohin da suke.

Mista Egbetokun ya ce rundunar ta ɗauki matakin ne don tabbatar da an yi zanga-zangar cikin kwanciyar hankali da lumana.

“Za mu tabbatar da ‘yancin da kundin tsarin mulki ya bai wa ‘yan Najeriya na taruwa don gudanar da zanga-zangar lumana,” in ji shi.

“Domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, muna kira ga duka ƙungiyoyin da ke sha’awar shiga zanga-zangar, su gabatar da cikakkun bayanansu da kwamishinonin ‘yansandan jihohin da za su yi zanga-zangar”.

Bayanan da Babban Sifeton ‘Yansandan ya buƙaci masu son shiga zanga-zangar su gabatar sun haɗa da:

  • Wurin da za su taru da hanyoyin da za su bi.
  • Lokacin da suke tunanin za su ɗauka suna yi
  • Sunaye da lambobin wayar jagororin da suka shirya zanga-zangar.
  • Matakan hana shigar ɓata-gari cikin zanga-zangar.
  • Gano waɗanda za su iya tayar da fitana a lokacin ta.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp