fidelitybank

Abun takaici ne ‘yan takara su yi amfani da addini da kabilanci a Kaduna – Hunkuyi

Date:

Sanata Suleiman Hunkuyi, dan takarar gwamna na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a jihar Kaduna, ya bayyana damuwarsa kan yadda ‘yan takara ke amfani da addini da kabilanci wajen jan hankalin jama’a a zaben gwamnan jihar da za a gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Ya kuma caccaki wasu kungiyoyin addini da suka amince da wasu ‘yan takarar gwamna, inda ya bayyana lamarin a matsayin wani mummunan lamari ga makomar dimokradiyya.

Ya ce yin amfani da addini ko kabila a jaha mai sarkakiya kamar Kaduna wajen yakin zabe yana da hadari.

Karanta Wannan: Ku guji siyasar kudi ‘yan Kaduna – Sanata Hunkuyi

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna a ranar Asabar din da ta gabata, dan takarar gwamnan ya shawarci wadanda suka cancanci kada kuri’a da su kaurace wa siyasa mai raba kan jama’a, su zabi sahihin dan takara da zai ciyar da jihar gaba a dukkanin bangarori na rayuwa.

Ya yi bayanin cewa ya yi imani da gwamnatin da ta kunshi kowa da kowa, ba tare da la’akari da shekaru, addini da kabila ba idan aka zabe shi a matsayin gwamna, yana mai jaddada cewa ita ce kadai hanyar da za a tabbatar da dorewar zaman lafiya a jihar.

A cewarsa, “Ina jin kuna sane da wata wasikar da shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen Jihar Kaduna ya rubuta, wadda ta amince da dan takarar gwamnan PDP. Muna kuma da wani faifan sauti inda wasu malaman addinin Musulunci suma suka amince da dan takarar jam’iyyar APC a zaben gwamna a jihar Kaduna.”

Ya yi mamakin inda jama’a za su dosa a lokacin da gwamnan da zai fito bayan zabe za a yi wa lakabi da gwamnan kiristoci ko na musulmi a wata babbar jiha kamar Kaduna.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp