Sanata Suleiman Hunkuyi, dan takarar gwamna na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a jihar Kaduna, ya bayyana damuwarsa kan yadda ‘yan takara ke amfani da addini da kabilanci wajen jan hankalin jama’a a zaben gwamnan jihar da za a gudanar a ranar 18 ga watan Maris.
Ya kuma caccaki wasu kungiyoyin addini da suka amince da wasu ‘yan takarar gwamna, inda ya bayyana lamarin a matsayin wani mummunan lamari ga makomar dimokradiyya.
Ya ce yin amfani da addini ko kabila a jaha mai sarkakiya kamar Kaduna wajen yakin zabe yana da hadari.
Karanta Wannan: Ku guji siyasar kudi ‘yan Kaduna – Sanata Hunkuyi
Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna a ranar Asabar din da ta gabata, dan takarar gwamnan ya shawarci wadanda suka cancanci kada kuri’a da su kaurace wa siyasa mai raba kan jama’a, su zabi sahihin dan takara da zai ciyar da jihar gaba a dukkanin bangarori na rayuwa.
Ya yi bayanin cewa ya yi imani da gwamnatin da ta kunshi kowa da kowa, ba tare da la’akari da shekaru, addini da kabila ba idan aka zabe shi a matsayin gwamna, yana mai jaddada cewa ita ce kadai hanyar da za a tabbatar da dorewar zaman lafiya a jihar.
A cewarsa, “Ina jin kuna sane da wata wasikar da shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen Jihar Kaduna ya rubuta, wadda ta amince da dan takarar gwamnan PDP. Muna kuma da wani faifan sauti inda wasu malaman addinin Musulunci suma suka amince da dan takarar jam’iyyar APC a zaben gwamna a jihar Kaduna.”
Ya yi mamakin inda jama’a za su dosa a lokacin da gwamnan da zai fito bayan zabe za a yi wa lakabi da gwamnan kiristoci ko na musulmi a wata babbar jiha kamar Kaduna.