Tsohon dan majalisa kuma fitaccen dan fafutuka, Shehu Sani, ya ce gwamnatin Najeriya ta kori ma’aikatan da suka kammala karatu a jami’o’in jamhuriyar Benin.
Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a asusunsa na X a ranar Litinin.
Sanata Sani, wanda bai bayyana dalilin sallamar ba, ya fuskanci kaduwa.
“Abin bakin ciki ne da karanta wasikun dakatar da wasu ma’aikatan FG da suka kammala karatu a jami’o’i a Jamhuriyar Benin,” in ji Sani a wata sanarwa da ya fitar.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun takardar shedar karya daga Jami’o’in Benin a farkon wannan shekarar.
Tun a baya dai dan jaridan Najeriya, Umar Audu ya bayyana yadda ya sayi takardar shaidar kammala karatun jami’ar Benin da N600,000.
Sakamakon haka, gwamnatin Najeriya ta sanar da dakatar da karatun digiri daga jami’o’in Benin da sauran su.
Tun da farko dai gwamnatin Najeriya ta saka sunayen jami’o’in kasashen waje 18 a Najeriya.