fidelitybank

Abun takaici ne dalibai na zaman gida na watanni 6

Date:

Shugaban kungiyar dalibai ta kasa (NANS), Umar Faruk Lawal ya ce, abin takaici ne ganin daliban jami’a suna zaune a gida sama da watanni 6.

Lawal ya bayyana haka ne ta wata sanarwa da aka rabawa DAILY POST da yammacin ranar Asabar.

An gudanar da zaben NANS a wurare biyu daban-daban a Abuja ranar Asabar.

Rahotanni sun ce shugabannin bangarorin biyu sun hada da Umar Faruk Lawal da Usman Umar.

Lawal dalibi ne a Sashin Laburare da Kimiyyar Watsa Labarai na Jami’ar Bayero Kano, yayin da Umar kuma dalibi ne a Jami’ar Tarayya ta Dutse, Jihar Jigawa.

Da yake jawabi bayan fitowar sa, Lawal ya bayyana cewa abin takaici ne yadda dalibai suka zauna a gida tsawon watanni shida sakamakon yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) suka shiga.

Sai dai Lawal ya ce NANS a karkashin jagorancinsa a shirye take ta zama sahihiyar muryar daliban a wannan tattaunawa na kawo karshen yajin aikin ASUU.

Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba NANS da ke karkashin sa za ta hadu da ASUU domin kawo karshen yajin aikin da malaman jami’o’in suka yi na tsawon watanni 7.

Shugaban kungiyar NANS ya kuma yi alkawarin cewa kungiyar ba za ta kara shiga harkokin siyasa ba.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp