fidelitybank

Abun takaici ne a kan rashin tsaron Najeriya – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana damuwarsa kan karuwar rashin tsaro a Najeriya.

Da yake tsokaci kan lokacin da ya ke kan karagar mulki, tsohon shugaban kasar ya ce batun tsaro shi ne babban abin da ya sa a gaba a lokacin gwamnatinsa, inda ya bukaci shugabanin da ke ci a yanzu da su dauki kwararan matakai na yaki da matsalar da ke kara ta’azzara.

Da yake magana a wata ziyara da ya kai Bauchi a ranar Lahadin da ta gabata, inda ya gana da Sarkin, Dokta Rilwanu Adamu, Obasanjo ya ce magance matsalar rashin tsaro na bukatar hadin kan shugabannin kananan hukumomi, saboda da yawa masu aikata laifuka suna rayuwa ne a cikin al’umma.

Kalamansa “A lokacin da muke mulki, mun ba da fifiko kan tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin kasar nan. A yanzu, muna buƙatar yin wani abu cikin gaggawa game da wannan.

“Mafi kyawun tsarin tsaro shine aikin ‘yan sandan al’umma domin kowa ya san makwabtansa a cikin al’umma. Da wannan, abu ne mai sauqi a gane muggan qwai.”

“Ina kira ga cibiyoyin gargajiya da su shigo tare da karfafa aikin ‘yan sanda a cikin muhallinsu domin rage yawan aikata laifuka”

“Lokacin da muke yi wa kasa hidima, mun yi komai a dunkule, an yanke shawarar mu tare domin a mai da hankali iri daya. Yayana Ahmed Adamu Mu’azu yana nan zaune kuma zai ba ni shaida. Duk abin da muka samu a lokacin, kokari ne na hadin gwiwa.”

Ya kara da cewa “Muna bukatar zaman lafiya, hadin kai da goyon bayan hadin kai a kasar nan idan har ya zama dole mu ci gaba. Abubuwa na iya sake zama daidai kuma a cikin kasar, abin da ya kamata mu yi shi ne mu hada kai mu yi al’amura tare.”

Tun da farko gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya shaidawa majalisar sarakunan gargajiya cewa tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya ziyarci jihar ne domin murnar nasarar da gwamnatinsa ta samu.

Ya kara da cewa, a yayin ziyarar, tsohon shugaban kasar zai kaddamar da wasu ayyuka guda biyu da aka kammala a karkashin gwamnatinsa, da nufin inganta ci gaban jihar da kuma saukaka harkokin sufuri.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp