fidelitybank

Abun kunya ne yadda ake samar da wuta mai karfin 4.5 a Najeriya – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya ce abin kunya ne yadda Najeriya ke samar da wutar lantarki mai karfin 4.5GW duk da fadin kasar.

Tinubu ya yi wannan jawabi ne a lokacin da yake kaddamar da wani taro mai mambobi 31 na shugaban kasa kan tattalin arziki a zauren majalisar da ke fadar shugaban kasa a Villa Abuja jiya.

Ya jaddada bukatar samar da sabbin hanyoyin magance kalubalen tattalin arzikin kasar.

A cewar Tinubu: ”Muna da kalubalen tsaron makamashi a Najeriya. Ya kamata mu hada hannu wajen inganta harkar man fetur da iskar gas, haka nan kuma mu kara samar da wutar lantarki da rarrabawa a fadin kasar nan.

“Mun kuduri aniyar yin hakan tare da hadin kan ku, hadin gwiwa, da shawarwarinku. A matsayinmu na kasa, abin kunya ne har yanzu muna samar da wutar lantarki mai karfin 4.5GW.

“Dole ne mu kara yawan man da muke hakowa zuwa ganga miliyan biyu (2) a kowace rana a cikin ‘yan watanni masu zuwa kuma mun kuduri aniyar kawar da duk wani shingen shiga zuba jari a bangaren makamashi tare da kara yin gasa.”

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp