Allah ya yiwa wata amarya mai suna Hauwa Abdullahi Shehu wacce ake kira da Ummi rasuwa washe garin aurenta.
An dai daura auren Ummi ne a ranar Asabar, 5 ga watan Fabrairu, amma sai ta ce ga garinku nan bayan nan Labarin mutuwarta ya taba zukatan mutane sosai a shafin soshiyal midiya, inda suka yi mata addu’o’in samun rahmar Allah.
An daura auren amaryar mai suna Hauwa Abdullahi Shehu wacce ake kira da Ummi da angonta ASP Abdulmuhyi Bagel Garba a yankin Azare dake jihar Bauchi.