fidelitybank

Abun damuwa ne matuka na karancin sayen kujerun Hajji – Hukumar Alhazan Kano

Date:

Shugaban hukumar alhazan jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya nuna damuwarsa kan ƙarancin sayen kujerun aikin Hajji mai zuwa.

Shugaban ya bayyana hakan ne a yau Talata yayin wani taron haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatan hukumar da da kuma manyan jami’anta na ƙananan hukumomi, a ofishin hukumar da ke Kano, kamar yadda wata sanarwa da kakakin hukumar Sulaiman A. Dederi ya fitar ta bayyana.

Alhaji Lamin ya buƙaci shugabannin hukumar na ƙananan hukumomi da su tashi haiƙan su ƙara azama wajen ganin an sayar da yawan kujerun da aka ware wa yankunansu.

Haka kuma ya yi kira da a samar da dabaru na bunƙasa cinikin kujerun da cimma aikin da ke gaban jihar a kan lokaci.

Hukumar alhazan ta sanya ranar 1 ga watan Janairu na shekara mai kamawa, 2025, a matsayin ranar rufe karɓar kuɗin ajiya na aikin Hajjin na bana daga maniyyata a jihar.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp