fidelitybank

Abun da ya sanya ba mu fara biyan alawus ɗin dubu 77 ba – NYSC

Date:

Hukumar yi wa ƙasa hidima ta NYSC, ta ce dalilin da ya sa aka samu jinkirin fara biyan sabon ƙarin alawus ɗin masu yi wa ƙasa hidima, shi ne gwamnati ba ta sakar wa hukumar kuɗin sabon ƙarin ba.

A tattaunawarsa da BBC, shugaban hukumar Birgediya Janar Yus’au Dogara Ahmed, ya ce a hukumance sun samu takardar amincewa da ƙarin, amma ba a riga aka sakar wa hukumar kuɗin ba.

”Ai ba ma su kaɗai ba, har ma’aikatan hukumarmu suma an yi musu ƙarin, su kan nasu ma ya kai kusan wata huɗu zuwa biyar, amma ba a fara biyansu ba, amma muna sa rai nan ba da jimawa ba, za a fara biya, amma bai riga ya zo hannunma ba tukunna”, in ji.

”Bayanin da muka samu ba a ce mana cewa yaushe za a fara biya ba, amma dai an tabbatar mana cewa an yi musu ƙari daga ranar 29 ga watan Yulin 2024”, kamar yadda ya yi ƙarin haske.

A cikin watan da ya gabata ne hukumar NYSC ta fitar da sanarwa yin ƙari a alawus ɗin masu yi wa ƙasa hidima daga naira 33,000 zuwa 77,000.

Sanarwar ta ce ƙarin sabon alawus ɗin zai fara aiki ne daga watan Yulin wannan shekarar, abin da ke nuna cewa masu yi wa ƙasa hidimar za su samu ariyas na aƙalla wata uku.

To sai dai da dama daga cikin masu hidimar ƙasar sun saka rai da ganin ƙarin a alawus ɗin a watan da ya gabata.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp