fidelitybank

Abun da ya sa na bar PDP – Shema

Date:

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Barr Ibrahim Shehu Shema, ya ce rashin adalcin da ka yi masa ne ya sanya shi ficewa daga jam’iyyarsa ta PDP.

Cikin wata tattaunawa da BBC, tsohon gwamnan ya ce ya fice daga jam’iyyar ne tun shekarar da ta gabata, bayan ta dakatar da shi tare da Ayo Fayose da Anyim Pios Ayim ba tare da bayyana musu dalilin hakan ba.

”Amma kuma abin haushin shi ne ni kaÉ—ai ne a ciki aka ce an dakatar da zaÉ“aɓɓun shugabannin jam’iyyar daga mazaÉ“ata”, in ji tsohon gwamnan.

”Kan hakan ne na rubuta takarda zuwa ga Party Chaiman na ce ba a bi Æ™a’ida ba wajen dakatar da ni tare da shugabannin jam’iiyar mazaÉ“ar tawa ba, saboda a matsayina na jigo a jam’iyyar wanda ya taÉ“a riÆ™e mukamin mataimakin jam’iyyar mai kula da jihohin arewa 19, na riÆ™e muÆ™amin shugaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar a lokacin, hasalima ni na bijiro da hanyoyi da dabarun ladabtarwa na jam’iyyar, amma aka wayi gari da dakatar da ni ba tare da bayyana min laifin da na aikata ba”, in ji Shema.

”Shi ya sa a cikin takardar da na rubuta na bayar da wa’adin sa’o’i 48 da cewa a bayyana min laifin da na aikata, ni da zaÉ“aɓɓun shugabannin jam’iyyar na mazaÉ“ar har aka É—auki matakin dakatarwar, idan ba a yi ba to zan fice daga jam’iyyar”, in ji tsohon gwamnan

Toshon gwamnan na Katsina ya ce bayan kwana uku ne sai jam’iyyar ta ce ta janye dakatarwar da ta yi masa tare da Ayo Fayose da Anyim Pios Ayim, amma kuma ban da sauran zaÉ“aɓɓun shugabannin jam’iyyar da aka dakatar É—in ba.

Barister Shema ya ce rashin mayar da su zaÉ“aɓɓun shugannin jam’iyyar mazaÉ“ar ne ya sa ya fice daga jam’iyyar.

A baya-bayan nan ne dai, Shema ya yanki katin jam’iyyar APC a mazaɓarsa ta Shema cikin ƙaramar hukumar Dutsin-ma.

Barr Ibrahim Shehu Shema ya mulki jihar na tsawon wa’adi biyu Æ™arÆ™ashin jam’iyyar ta PDP.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp