fidelitybank

Abun da Ronaldo ya yi wa Tan Hag rashin da’a ne – Leboeuf

Date:

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Frank Leboeuf ya yabawa Erik ten Hag saboda hukunta Cristiano Ronaldo da ya yi.

A cewar Leboeuf, wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or sau biyar ya riga ya yi tunanin ya fi kocin, lura da cewa ko da yaushe dan Portugal din ya kan girgiza da nuna alamun a duk lokacin da ba ya filin wasa.

Ronaldo dai ba a cikin ‘yan wasan da suka tashi kunnen doki 1-1 da Chelsea a karshen mako a matsayin hukuncin da ya bijire wa kocinsa da kuma rashin mutunta abokan wasansa.

Amma Ten Hag ya sanar a ranar Laraba cewa dan wasan mai shekaru 37 ya koma kungiyar gabanin wasan da za su fafata a gasar cin kofin zakarun Turai ranar Alhamis.

Leboeuf ya yi imanin cewa kocin dan kasar Holland ya yi rawar gani wajen yanke hukunci ga Ronaldo, inda dan kasar Portugal din ya maimaita irin wannan abu a wasan da Man United ta buga da Rayo.

Tsohon dan wasan na Chelsea ya ce rashin da’a ne dan wasan kwallon kafa irin Ronaldo ya rika yin hakan kuma a koda yaushe yana nunawa duniya yana fushi.

Leboeuf ya shaida wa FairBettingSites cewa “Hakanan rashin kwarewa ne kuma don hakan ya sake faruwa a kan Tottenham, ina tsammanin ba za ku iya yin hakan ba, kuma ya san ainihin abin da yake yi kuma yana so ya nuna wa duniya cewa bai ji dadi ba.”

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An yi wa Dan shekara 7 yankan Rago a Kano

Wasu ɓata gari da ba a san ko su...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Rundunar Æ´an sanda ta jihar Kano ta ce, ta...
X whatsapp