fidelitybank

Abun a yaba wa gwamnan Osun ne yadda ya bijire kan hana shi zabe – Atiku

Date:

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke bisa gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar, duk da gwamnatin tarayya da ƴansanda sun buƙaci a dakatar da zaɓen.

Tun da farko dai ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi ne ya yi kira ga gwamnan jihar da ya dakata da zaɓen, domin a cewarsa, wa’adin tsofaffin ƙananan hukumomin bai ƙare ba.

Sannan kuma ƴansanda sun yi gargaɗin cewa a dakata da gudanar da zaɓen saboda hukuncin wata kotu, da kuma bayanin sirri da suka samu kan yiwuwar tayar da hargitsi.

Sai dai alamu sun nuna gwamnan ya yi watsi da gargaɗin, inda mutanen jihar suka fito domin kaɗa ƙuri’a a zaɓen.

Domin haka ne Atiku ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce, “a daidai lokacin da mutanen jihar Osun suka fito domin kaɗa ƙuri’ar zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi, ina sake kira gare su da gudanar da zaɓen cikin lumana. Shugabannin ƙananan hukumomin su ne ƙashin bayan dimokuraɗiyya saboda kusancinsu ga al’umma.

“Ina yaba wa gwamnan Osun Ademola Adeleke bisa gudanar da zaɓen, sannan ina kira ga jami’an tsaro da masu sanya ido a akwatunan zaɓe su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa.”

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp