Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke bisa gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar, duk da gwamnatin tarayya da ƴansanda sun buƙaci a dakatar da zaɓen.
Tun da farko dai ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi ne ya yi kira ga gwamnan jihar da ya dakata da zaɓen, domin a cewarsa, wa’adin tsofaffin ƙananan hukumomin bai ƙare ba.
Sannan kuma ƴansanda sun yi gargaɗin cewa a dakata da gudanar da zaɓen saboda hukuncin wata kotu, da kuma bayanin sirri da suka samu kan yiwuwar tayar da hargitsi.
Sai dai alamu sun nuna gwamnan ya yi watsi da gargaɗin, inda mutanen jihar suka fito domin kaɗa ƙuri’a a zaɓen.
Domin haka ne Atiku ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce, “a daidai lokacin da mutanen jihar Osun suka fito domin kaɗa ƙuri’ar zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi, ina sake kira gare su da gudanar da zaɓen cikin lumana. Shugabannin ƙananan hukumomin su ne ƙashin bayan dimokuraɗiyya saboda kusancinsu ga al’umma.
“Ina yaba wa gwamnan Osun Ademola Adeleke bisa gudanar da zaɓen, sannan ina kira ga jami’an tsaro da masu sanya ido a akwatunan zaɓe su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa.”