Babban birnin tarayya Abuja da jihar Legas na fuskantar katsewar wutar lantarki, sakamakon wani rugujewar wutar lantarki ta kasa.
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Abuja (AEDC), a wata sanarwa da ta rabawa abokan huldarsa ta shafinta na Twitter, ta dora laifin rashin wutar lantarkin a kan gazawar wutar lantarki da ta afku a Yammacin ranar Juma’a.
“Don Allah a sanar da ku cewa katsewar wutar lantarki a halin yanzu ya faru ne, sakamakon gazawar tsarin daga National Grid. Tsarin ya ruguje ne da misalin karfe 6.30 na yamma da kuma karfe 8.50 na Yamma a yau 8 ga Afrilu 2022, lamarin da ya sa ake fama da matsalar a halin yanzu, ”in ji sanarwar.