fidelitybank

Abubuwan da za su iya faru a 2024

Date:

Mafi yawan sassan duniya sun shiga sabuwar shekara ta 2024, sai dai abubuwan da shekarar mai yiwuwa ta tanadar wa rayuwar al’umma.

Ga wasu jerin abubuwan da ake sa ran za su iya faruwa:

Janairu– Gasar cin Kofin Afirka wadda Ivory Coast za ta karɓi baƙunci, za ta kankama.

Fabrairu– Kamar kullum za mu iya sa ran ganin Sabuwar Shekarar Gargajiya a wasu ƙasashe na faɗin duniya (kamar wadda aka fi sani da sabuwar shekarar al’ummar China)

Maris– Vladimir Putin, mutumin da ya jagoranci Rasha a matsayin firaminista da kuma shugaban ƙasa tun 1999, zai sake tsayawa takara a wa’adi na biyar.

Afrilu– Mutane a Amurka za iya ganin kusufin wata na ƙarshe a ƙasar cikin sama da shekara 20, wanda akan yi shagulgula a Arkansas.

A Afrilu zuwa Mayu muna kuma sa ran ganin babban zaɓen Indiya.

Mayu– Kumbon zuwa duniyar wata na China mai suna Chang’e-6 zai yi ƙoƙarin tattaro sama da kilogram biyu na samfura daga sashen duhu na Wata.

Yuni– Mata biyu za su shiga takarar shugaban ƙasa a Mexico yayin da kuma za a buɗe Gasar cin Kofin Turai na UEFA Euro 2024 a Jamus. Sai Gasar cin Kofin Duniya na wasan Kurket mai taken T20 wanda Amurka za ta karɓi baƙunci.

Yuli– Za a fara wasannin Olympic na birnin Paris.

Agusta– Za a fara gasar tseren mata ta Tours de France a Netherlands kuma a kawo ƙarshe a Faransa.

Oktoba– Rasha za ta karɓi baƙuncin babban taron BRICs a kudu maso yammacin birnin Kazan.

Nuwamba– Ma’aikatan farko na kumbon zuwa duniyar wata a cikin shekara 52, ‘yan sama jannati huɗu za su tafi zuwa sararin wata tsawon kwana goma.

Za a yi zaɓen shugaban ƙasa a Amurka, kuma ga dukkan alamu za a sake fafata takara ne tsakanin Joe Biden da kuma Donald Trump ne. In ji BBC.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp