fidelitybank

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

Date:

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu, ƙarƙashin jagorancin Barrister Aminu Hussaini ya miƙa rahoton bincikensa ga sakataren gwamnatin jihar.

Wasu daga cikin manyan batutuwan da kwamitin ya gano sun haɗa da:

Kwamishinan ya amince ya tsaya wa mai lefin domin raɗin kansa a ranar 18 ga watan Yulin 2025.
Rantsuwa: Ibrahim Namadi ya yi rantsuwa kan belin a matsayinsa na kwamishina mai ci kuma ya yi alƙawarin cika dukkan sharuɗɗan beli har zuwa ƙarshen shari’ar.
Namadi ya fahimci cewa kwamishina kuma ɗan majalisar zartarwa na jiha ne kawai zai iya tsaya wa wani a harkar shari’ar bisa tanade-tanaden sharuɗɗan kotu.
Namadi bai yi takatsantsan ba: Kwamishinan bai yi takatsantsan ba kafin ya ɗauki wannan matsaya ta tsaya wa wani da ake zargi da laifi da ke fuskantar babbar tuhuma da ta jiɓanci safarar ƙwaya.
Kwamishinan yana da cikakkiyar masaniyar haƙiƙanin girman tuhumar da ake yi wa mutumin da ta jiɓanci safarar ƙwaya.
‎Namadi ya saɓa dokokin gwamnatin Kano dangane da matsayarta da ke fili ta ƙyamar safarar ƙwaya da ta’ammali da ƙwayar da ɓata matasa da sauran laifuka da suka jiɓance su.
‎Babu shaidar da ke nuna kwamishinan na da wata alaƙa da wanda ake tuhumar kafin yanzu.
‎Kwamitin bai samu wata shaidar da ke nuna yin amfani da kuɗi ko wata kadara ba domin jan hankalin kwamishinan kafin ya aikata belin.
Kwamishinan bai ajiye ko kwabo ba na beli ciki kuwa har da naira 5,000,000 da ake magana akai. Wannan kawai yana ƙunshe ne a cikin takardar rantsuwar da wanda ake tuhumar ya rubuta.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp