fidelitybank

Aboubakar ne gwarzon dan wasa a karawar Kamaru daSerbia – Gyang

Date:

Tsohon dan wasan Ghana Asamoah Gyang, ya bayyana Vincent Aboubakar a matsayin gwarzon dan wasan kwallon kafa bayan wasan da Kamaru ta buga da Serbia da ci 3-3 a gasar cin kofin duniya ranar Litinin.

A cewar Gyang, Aboubakar ya kasance tauraron dan wasan da aka fafata tsakanin Kamaru da Sabiya.

Aboubakar ya taka rawar gani lokacin da ya fito daga benci yayin da Kamaru ta tashi canjaras da Serbia.

Kamaru ta fara cin kwallo ta hannun Jean-Charles Castelletto kafin Serbia ta rama kwallaye uku daga hannun Strahinja Pavlovic, Sergej Milinkovic-Savic, Aleksandar Mitrovic.

Sai dai kwallaye biyu da Aboubakar da Eric Maxim Choupo-Moting suka ci ne suka tabbatar da cewa kungiyoyin biyu sun tashi canjaras.

Da yake magana bayan wasan, Gyang ya ce a SuperSport: “Shi [Vincent Aboubakar] shine tauraron dan wasan. Shigowa yayi ya tabbatar da cancantarsa.

“Ya tabbatar da cewa shi ne wanda zai iya daukar kungiyar a kafadarsa, ya samu kwallo da taimako. A gare ni, shi ne mutumin da ya fi kowa wasa.”

Sakamakon ya nuna cewa Kamaru tana matsayi na uku a rukunin G da maki daya.

Yanzu haka dai kungiyar ta yammacin Afirka za ta kara da Brazil a wasansu na karshe na rukuni a ranar Juma’a.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...
X whatsapp