fidelitybank

Aboubakar ne gwarzon dan wasa a karawar Kamaru daSerbia – Gyang

Date:

Tsohon dan wasan Ghana Asamoah Gyang, ya bayyana Vincent Aboubakar a matsayin gwarzon dan wasan kwallon kafa bayan wasan da Kamaru ta buga da Serbia da ci 3-3 a gasar cin kofin duniya ranar Litinin.

A cewar Gyang, Aboubakar ya kasance tauraron dan wasan da aka fafata tsakanin Kamaru da Sabiya.

Aboubakar ya taka rawar gani lokacin da ya fito daga benci yayin da Kamaru ta tashi canjaras da Serbia.

Kamaru ta fara cin kwallo ta hannun Jean-Charles Castelletto kafin Serbia ta rama kwallaye uku daga hannun Strahinja Pavlovic, Sergej Milinkovic-Savic, Aleksandar Mitrovic.

Sai dai kwallaye biyu da Aboubakar da Eric Maxim Choupo-Moting suka ci ne suka tabbatar da cewa kungiyoyin biyu sun tashi canjaras.

Da yake magana bayan wasan, Gyang ya ce a SuperSport: “Shi [Vincent Aboubakar] shine tauraron dan wasan. Shigowa yayi ya tabbatar da cancantarsa.

“Ya tabbatar da cewa shi ne wanda zai iya daukar kungiyar a kafadarsa, ya samu kwallo da taimako. A gare ni, shi ne mutumin da ya fi kowa wasa.”

Sakamakon ya nuna cewa Kamaru tana matsayi na uku a rukunin G da maki daya.

Yanzu haka dai kungiyar ta yammacin Afirka za ta kara da Brazil a wasansu na karshe na rukuni a ranar Juma’a.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp