Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben shugaban kasa na badi, Bola Tinubu ya ce, abokan hamayyarsa a wasu jam’iyyu ba su da gaskiya.
Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Talata a garin Calabar na jihar Cross River, yayin wani taro da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC.
Ya ce yana da yakinin cewa jam’iyyar APC za ta lashe dukkan zabukan shekara mai zuwa, yayin da ya shaida wa dimbin jama’ar da ke ta murna cewa yana da duk abin da ya dace don ya ci zabe ya kuma mulki kasar nan.
“Ba su da baya; ba su da gogewa, ba su da tarihi, ba su da mutunci, don haka duk abin da suke yi sai cin zarafi da zagi. Damuwata ita ce ci gaban Najeriya, kuma abin da zan yi ke nan a matsayina na shugaban kasa,” inji shi.
Tinubu ya kara da cewa, “Laifinmu ne a kasar nan cewa shekaru 60 da suka gabata ba mu samu ci gaba ba, amma ciyar da Najeriya gaba abu ne da ya kamata a yi.”