Kungiyar dattawan Arewa, ta nuna fargabar cewa, ƙabilanci da kwaɗayi na barazanar kawo cikas ga ƙoƙarin farfadowar kasar a zaben 2023.
Kungiyar ta bayyana damuwa kan abubuwan da ke faruwa a bangarori da dama na siyasar Najeriya dangane da shirye-shiryen zaben 2023.
Wata sanarwa da daraktan Yada Labarai na kungiyar Dakta Hakeem Baba-Ahmed ya fitar a Abuja, ya zargi wasu ƴan siyasa da abun da ya kira ‘’amfani da addini wajen raba kan yan ƙasa’’
Ya ce, “Wadannan abubuwan da ke faruwa suna barazana ga tsarin dimokuradiyyar da muke amfani da shi. Siyasarmu a yanzu ta sauya daga yadda da ra’ayin juna, don haka za a girbi abun da aka shuka sakamakon kwadayin wasu daga cikin ‘yan siyasarmu da suka gaza nuna kyakkyawan jagoranci’’