fidelitybank

Abin takaici ne rashin kammala aikin hanyar Kano zuwa Abuja – NANS

Date:

Shugaban Kungiyar Dalibai ta Ƙasa (NANS), Sadi Garba Said, ya bayyana matuƙar takaicinsa da damuwa kan matakin da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka na dakatar da aikin gina hanyar Kano-Abuja.

Mal. Sa’id yana mai cewa wannan mataki babban koma baya ne ga al’ummar yankin.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa.

Sadi ya ce, “Dakatar da wannan aiki zai shafi tattalin arziki da walwalar jama’a sosai, kuma hakan yana nufin ƙarin wahala ga matafiya.”

Aikin, wanda aka fara tun 10 ga Fabrairu, 2021, an shirya kammala shi a ƙarshen 2023. Amma dakatarwar da aka yi kwatsam ta haifar da matsaloli, inda matafiya suka fara fuskantar wahalhalu irin su tsawaitar tafiya da tsadar sufuri.

Sadi ya nuna damuwa kan yadda dalibai da ke amfani da hanyar don zuwa makaranta ke fuskantar ƙalubale. “Daliban da ke dogaro da wannan hanya don tafiye-tafiye sun shiga halin ha’ula’i. Wannan yanayi ba zai iya ci gaba haka ba,” in ji shi.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta yi karin haske kan dalilin da ya sa aka dakatar da aikin tare da Julius Berger Nigeria Plc, tare da bayyana sabon shiri mai kyau na kammala aikin.

“Ba za mu yarda da ƙarin jinkiri ba. Gwamnati dole ta nuna gaskiya da amfani da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace,” Sadi ya jaddada.

Haka kuma, ya yi alkawarin cewa NANS Yankin A za ta ci gaba da sanya ido kan wannan lamari domin kare haƙƙi da walwalar al’umma. “Zamu tabbatar gwamnati tana cika alƙawuran da ta ɗauka kan wannan aiki domin ci gaban al’ummar mu,” ya ƙara da cewa.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp