fidelitybank

Abin takaici ne rashin kammala aikin hanyar Kano zuwa Abuja – NANS

Date:

Shugaban Kungiyar Dalibai ta Ƙasa (NANS), Sadi Garba Said, ya bayyana matuƙar takaicinsa da damuwa kan matakin da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka na dakatar da aikin gina hanyar Kano-Abuja.

Mal. Sa’id yana mai cewa wannan mataki babban koma baya ne ga al’ummar yankin.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa.

Sadi ya ce, “Dakatar da wannan aiki zai shafi tattalin arziki da walwalar jama’a sosai, kuma hakan yana nufin ƙarin wahala ga matafiya.”

Aikin, wanda aka fara tun 10 ga Fabrairu, 2021, an shirya kammala shi a ƙarshen 2023. Amma dakatarwar da aka yi kwatsam ta haifar da matsaloli, inda matafiya suka fara fuskantar wahalhalu irin su tsawaitar tafiya da tsadar sufuri.

Sadi ya nuna damuwa kan yadda dalibai da ke amfani da hanyar don zuwa makaranta ke fuskantar ƙalubale. “Daliban da ke dogaro da wannan hanya don tafiye-tafiye sun shiga halin ha’ula’i. Wannan yanayi ba zai iya ci gaba haka ba,” in ji shi.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta yi karin haske kan dalilin da ya sa aka dakatar da aikin tare da Julius Berger Nigeria Plc, tare da bayyana sabon shiri mai kyau na kammala aikin.

“Ba za mu yarda da ƙarin jinkiri ba. Gwamnati dole ta nuna gaskiya da amfani da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace,” Sadi ya jaddada.

Haka kuma, ya yi alkawarin cewa NANS Yankin A za ta ci gaba da sanya ido kan wannan lamari domin kare haƙƙi da walwalar al’umma. “Zamu tabbatar gwamnati tana cika alƙawuran da ta ɗauka kan wannan aiki domin ci gaban al’ummar mu,” ya ƙara da cewa.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp