Gwamna Bello Mohammed Matawalle na jihar Zamfara, ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da bikin Sallah na EID EL Kabir, wajen yin addu’ar samun zaman lafiya a jihar baki daya.
Matawalle, wanda ya yi kira ga mabiya addinin Musulunci da su yi addu’a ga Allah ya kawo musu dauki, ya ce, duk kokarin da gwamnatinsa ta yi na kawo karshen ‘yan fashi ya ci tura.
Ya ce ,babu wanda zai iya cimma wani abu mai ma’ana idan babu zaman lafiya.
A cewarsa, abin mamaki ne yadda gwamnatinsa ta gaji wannan munanan ci gaban, inda ya yi kira ga jama’a da su yi la’akari da matsalar tsaro da tattalin arziki da ayyukan ‘yan fashin suka kawo tare da tsara dabarun kawo karshen ayyukan ta’addanci.
Gwamnan ya bayyana haka ne a garin Maradun, mahaifar sa, inda ya yi bikin EID EL Kabir, inda ya yi kira ga kowa da kowa, ba tare da banbancin addini da siyasa ba, da ya hada karfi da karfe da gwamnatinsa domin yakar abokan gaba.
Ya ce gwamnatinsa ta yi duk abin da za ta iya domin kawo karshen munanan ci gaban amma ayyukan ‘yan fashin sun ci gaba.