Sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta yamma, Abdul’aziz Yari Abubakar, ya jajantawa wadanda harin da jirgin sama ya rutsa da su a garin Tungar-Kara da ke karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara.
Hare-haren na sama, wanda rahotanni suka ce an yi niyya ne domin kakkabe ‘yan bindigar da ke tserewa, ya yi sanadiyyar salwantar rayuka da dama da ba su ji ba ba su gani ba a kauyen.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun Al’mansoor Gusau, Darakta Janar na yada labarai ga Sanata Yari, Sanatan ya bukaci a kwantar da hankula, yayin da ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasu tare da yin addu’ar samun sauki cikin gaggawar wadanda suka jikkata.
Sanatan ya yi addu’ar Allah ya karbi marigayin a matsayin shahidai, ya ba su aljannah Firdausi.
Ya kuma yabawa sojoji bisa kokarin da suke yi na magance ‘yan fashin, amma ya bukaci a kara daukar matakan taka tsantsan a ayyukan da za a yi a nan gaba domin hana afkuwar asarar da ba a yi niyya ba.
Sanata Yari ya jaddada fatansa na samun zaman lafiya da ci gaba a jihar Zamfara da ma kasar baki daya.