fidelitybank

Abin da ya janyo tsaikon biyan maniyyatan Abuja kuɗin guzurinsu – Hukuma

Date:

Gaba a yau ne hukumar jin dadin alhazai reshen Abuja, ta ce, za ta ci gaba da aikin biyan maniyyatanta 2,958 da ke Saudiyya cikon kudin guzurinsu na dala 200.

Tun farko aikin ya gamu da cikas bayan da wasu daga cikin maniyyatan suka yi barazanar dukan jami’an da suka je raba kuɗaɗen tare da nuna rashin amincewarsu da cikon dala 200 a maimakon dala 300 da tun farko aka sanar za a cika masu lokacin jigilarsu zuwa kasa mai tsarki.

Mataimaki na musamman ga ƙaramar ministar Abuja shawara, Dr Abdullahi Isa Kauranmata wanda ya kira taron gaggawa domin tattauna ƙalubalen da maniyyatan babban birnin ke fuskanta, ya ce suna ƙoƙari domin ganin an sauƙaƙa wa maniyyata tare da inganta walwalarsu a ƙasa mai tsarki.

Ya ce “na ji korafinku game da kuɗin guziri kuma na nemi a fara biyanku kuɗaɗenku, amma abin mamaki sai na ji wasu na barazanar dukan jami’an da suka zo”.

Dakta Kauranmata ya bayyana cewa duka maniyyatan da aka ba su dala 500, gwamnatocin jihohinsu ne suka tallafa masu.

Ya ce sauyin da aka samu ya faru ne sakamakon hauhawar da dala take yi duk da cewa an sanar da kowane maniyyaci cewa za a bashi cikon dala 300.

A ranar Asabar ne dai wasu maniyyatan Abujan suka yi ƙorafin cewa hukumar alhazan birnin ta saɓa alƙawarin da ta yi musu na ba su kuɗin guzuri, bayan da hukumar ta ce ba za ta basu dala 300 da ta yi musu alƙawari tun da farko ba.

Dakta Kauranmata ya kuma yi alƙawarin nema wa maniyyatan sauki daga ministan babban birnin domin rage masu radadin da suke fuskanta.

Ya kuma yi magana kan matsalar jinkirin da maniyyata ke fuskanta inda ya yi alƙawarin za a samar da ma’aikatan lafiya da za su riƙa bai wa maniyyata marasa lafiya kulawa domin shirya wa babbar ibadar da ke tafe ta sauke aikin hajji.

Game da ƙorafin abinci da maniyyata ke yi, Dakta Kauranmata ya ce zai kai ziyara zuwa wurin da ake dafa abincin domin gani da ido da nufin cimma matsaya kan irin abincin.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp