Malamin makarantar da a ke zargi sace dalibarsa mai shekaru 5, Hanifa Abubakar, kuma ya kashe ta, Abdulmalik Tanko, ya musanta zargin kisan kai da ake tuhumarsa da shi.
Daily Nigerian ta rawaito cewa, gwamnatin jihar Kano ta shigar da kara tare da tuhumar sa, abubuwa biyar, a kan Tanko da wadanda suka taimaka masa, Hashimu Isyaku da Fatima Jibrin, a babbar kotu mai lamba 5 a jihar.
An gurfanar da su uku kan zargin hadin baki, garkuwa da mutum, boye wa da tsare wanda suka yi garkuwa da ita da kuma kisa, wanda sun ci karo da sashi na 97, 274, 277 da 221 na Penal Code.
Da aka karanto musu tuhumar da ake musu a ranar Litinin, sun musanta aikata abin da ake tuhamarsu da aikatawa.