Gwamnatin jihar Kano za ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje a gaban kotu, bisa zargin karkatar da kudaden jihar da kuma karkatar da kadarorin jihar.
Wani sammacin kotu da wakilinmu ya gani ya nuna cewa Ganduje za a gurfanar da shi ne tare da matarsa, Hafsat, da wasu mutane shida a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume takwas da suka hada da cin hancin dala, da karkatar da wasu kudade da suka hada da $413,000 da kuma N1.38. biliyan.
Sauran wadanda ake karar sun hada da Abubakar Bawuro, Umar Abdullahi Umar, Jibrilla Muhammad, Lamash Properties Ltd, Safari Textiles Ltd da Lesage General Enterprises.
Gwamnatin jihar Kano, a tuhumar da ake yi wa Ganduje da sauran wadanda ake kara, ta ce ta tattara shaidu 15.
An dage sauraren karar zuwa ranar 17 ga Afrilu, 2024, domin gurfana a gaban mai shari’a Malam Na’aba na babbar kotun jihar Kano.