fidelitybank

Abba ya ɗaukaka ƙara mai hujjoji 43 na ƙalubalantar nasarar Gawuna

Date:

Gwamnan Kano, da kotun zaɓen jihar ta soke nasararsa, Abba Kabir Yusuf, ya miƙa shari’arsa gaban kotun ɗaukaka ƙara, inda yake ƙalubalantar hukuncin na ranar 20 ga watan Satumba.

Wata takardar kotu mai kwanan watan 2 ga watan Oktoban 2023, ta nuna cewa Gwamna Abba Kabir ya zayyana Hukumar zaɓe ta INEC da jam’iyyar APC da kuma jam’iyyarsa ta NNPP, a matsayin waɗanda yake da ƙorafi a kansu.

Mai ƙorafin a cewar takardarn kotun, bai gamsu da hukuncin alƙalan kotun ƙararrakin zaɓen gwamnan Kano ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay ta yanke ba.

Kotun dai ta soke ƙuri’a 165,633 daga cikin 1,019,602 da aka kaɗa wa Abba Kabir Yusuf a zaɓen 18 ga watan Maris, bisa hujjar cewa ba halattattun ƙuri’u ba ne, saboda ba su da hatimi da kwanan wata.

Don haka, kotun ta ayyana Nasir Yusuf Gawuna a matsayin halastaccen gwamna, ta kuma umarci hukumar zaɓe ta janye shaidar cin zaɓen da ta bai wa Abba Kabir Yusuf tun da farko, sannan ta bai wa Gawuna shaidar nasara.

Sai dai Abba Kabir a yanzu ya ƙalubalanci matakin, inda ya yi iƙirarin cewa hukuncin ƙaramar kotun cike yake da kura-kurai, har ma ya kafa hujjoji guda 43.

Cikin buƙatun da gwamnan na jam’iyyar NNPP ya nema a gaban kotun ɗaukaka ƙara, har da ta neman jingine hukuncin kotun sauraron zaɓen gwamnan Kano, sannan ta kori ƙarar da jam’iyyar APC ta shigar tun da farko.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp