fidelitybank

Abba ya siyawa ‘yan majalisa 41 motoci kowacce naira miliyan 68

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da siyan motocin guda 41, akan kudi Naira miliyan 68 ga ‘yan majalisar dokokin jihar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, gwamnatin jihar Kano ta bakin shugaban ma’aikatan gwamnan jihar, Alhaji Shehu Wada Sagagi, ya ce hakki ne na ‘yan majalisar su samar da motocin aiki masu inganci.

An ce ‘yan majalisar sun riga sun mallaki motocin SUV, adadinsu ya kai kimanin Naira biliyan 2.6.

A cewar shugaban ma’aikatan, gwamnan ya yi la’akari da yanayin tattalin arziki, ya ba da umarnin a sa dan kwangilar ya fahimci bukatar yada kudaden na wani lokaci.

Sagagi ya jaddada cewa matakin gwamnan ya ta’allaka ne kan mutunta hakki da hakkokin dukkan bangarorin gwamnati.

Ya kara da cewa gwamnan ya ci gaba da jajircewa wajen ganin an samu zaman lafiya a kowane bangare na gwamnati da kuma al’ummar jihar baki daya.

Wani fitaccen dan majalisar da ya yi magana da manema labarai bisa sharadin sakaya sunansa, ya kuma kare sayen motocin SUV din.

‘’Me ya sa kuke yin tsauni daga tudun mole kan siyan sababbin motoci ga ‘yan majalisa? Haka kuma gwamnatocin da suka gabata a jihar sun yi,” in ji shi yayin da yake mayar da martani game da cece-kucen da ake ta samu na sayen motocin.

Da aka tunatar da cewa lamarin ba haka yake ba duba da irin kalubalen da kasar nan ke fuskanta a fannin tattalin arziki, dan majalisar ya ce, “Shin kun gane cewa motar za ta saukaka ayyukan sa ido a kanmu kuma za a yi amfani da ita wajen gudanar da wasu ayyukan majalisa?

Majiya mai tushe ta bayyana cewa tun da farko Gwamna Abba Kabir Yusuf bai damu da sayen motocin ga ‘yan majalisar ba, sai dai manyan jami’an majalisar sun roke shi, inda suka ce suna bukatar sabbin motoci.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp