Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya naɗa fitaccen tauraron fina-finan Hausa na Kannywood, Sani Musa Danja a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin matasa da wasanni.
Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwaman jihar Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Lahadi, ya ce gwamnan ya amince da naɗin Sani Danja tare da wasu mutane da shugabannin hukumomin da aka sauya wa ma’aikatu da masu bai wa gwamna shawara.
A mako mai ƙarewa ne dai gwamnan na jihar Kanon ya yi wa majalisar zartarwarsa garambawul, inda ya sauke wasu ƙusoshin gwamnatinsa, cik har da sauke sakataren gwamnatin jihar da shugaban ma’aikatar fadar gwamnatinsa.