fidelitybank

Abba ya gabatar da ƙwarya-ƙwaryar kasafin Naira biliyan 24

Date:

Gwamnan jihar Kano ya sake gabatar da wani kwarya-kwaryan kasafin kudi ranar Talata na naira biliyan 24 a gaban majalisar dokokin jihar Kano don neman amincewarta.

Abba Kabir ya gabatar da rokon ne a cikin wata wasika da shugaban majalisar dokokin jihar, Isma’il Falgore ya karanta a zaman majalisar na yau.

Isma’il Falgore ya ce gwamnan ya nemi amincewar majalisar ne kamar yadda sashe na 122 karamin sashe na (A) da (B) na tsarin mulkin 1999 ya tanada.

Ya ce, “kudurin kwarya-kwaryan kasafin kudin na shekara ta 2023 a karo na byu, ya zama dole saboda wasu dalilai daga ciki har da kudaden da jihar ke sa ran samu daga kwamitin rabon kudade na asusun tarayya da harajin VAT da asusun kula da zaizayar kasa da harajin EMTL da kudaden rance na ayyukan samar da lantarki mai zaman kansa daga Babban Bankin Najeriya da kuma karin kudin shiga na cikin gida”.

Gwamnan ya ce bisa la’akari da wadannan bukatu da kuma muradin aiwatar da wasu muhimman ayyukan raya kasa na gaggawa a cikin jihar, an gabatar da kudurin kasafin kudin a kan bangarorin da suka hadar da biyan kudaden garatuti da naira biliyan hudu.

Akwai kuma kashe naira biliyan 20 a kan manyan ayyuka.

A cewarsa da karin kwarya-kwaryan kasafin kudin naira biliyan 58 da kuma na naira biliyan 24, kasafin kudin jihar Kano na shekara ta 2023 a yanzu ya kai naira biliyan 350.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...
X whatsapp