fidelitybank

Abba ka tsaya da ƙafafun ka ni dai na fita daga Kwankwasiyya – Sanata Ali Madakin Gini

Date:

Mataimakin shugaban marasa rinjaye a Majalisar Wakilai, Ali Sani Madakin Gini ya tabbatarwa da BBC cewa ya fita daga tsagin Kwankwasiyya a cikin jam’iyyarsa ta NNPP.

Ɗan majalisar mai wakiltar Dala a tsakiyar birnin Kano ya tabbatar da haka ne bayan wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta wanda a ciki aka ji yana cewa “Daga yau, na daina harkar Kwankwasiyya”.

A cikin bidiyon Ali Madakin Gini ya bayyana cewa “Kwankwasiyya ƙarya ce, Kwankwasiyya yaudara ce”.

Ya ƙara tabbatarwa da BBC cewa: “Na fahimci cewa an gina tafiyar Kwankwasiyya ce kawai domin ci gaban Kwankwaso”.

Zuwa yanzu dai ba a ji wani martani daga ɓangaren Sanata Kwankwaso ba a kan wannan ikirari.

Shi dai Ali Madaki ya ce har yanzu yana nan a jam’iyyarsa ta NNPP, amma ba tsagin jagorancin Sanata Rabi’u Kwankwaso ba.

Matakin na zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin jihar Kano, wanda jam’iyyar NNPP ta lashe dukkan kujerun.

An jiyo Ali Madakin Gini yana yaba wa gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, da cewa shi mutumin kirki don haka ya shawarce shi da ya yi duk yadda zai yi, ya tsaya da ƙafarsa.

A kwanan baya ne dai wata ƙungiya ta ɓullo a fagen siyasar Kano mai taken ‘Abba Tsaya da Ƙafarka’ mai rajin gwamnan na Kano ya daina biyayya ga jagoran Kwankwasiyya, ya ci gashin kansa, lamarin da ya janyo jam’iyyar NNPP a Kano ta dakatar da Sakataren Gwamnatin Kano da wani kwamishina, bisa zarginsu da alaƙa da ƙungiyar

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp